
Kungiyar Amurka na ci gaban kasashe USAID ta kaddamar da ayyuka a jihohin Najeriya daya kai kudi dalar Amurka naira miliyan 72 don inganta shugabanci.
Shirin zai inganta shugabancin jiha-jiha da suka hada da Adamawa, AkwaIbom, Bauchi, Ebonyi, Gombe da Sokoto da nufin bunkusa shi zuwa wasu jihohin.
Cikin sanarwa da USAID ta fitar a yau, na kunshe da cewa aikin jiha zuwa jiha na shekaru 5 zaiyi matukar taimakawa yadda jihohin shiyewa da kuma tsare-tsare dama bangaren kiwon lafiya, ilimi, samar da ruwa da sauran su.

Ambasadon Amurka a Najeriya Mary Beth Leonard tace aikin na nuna irin yadda kasar Amurka ke burin hada kai da Najeriya wajen inganta shugabanci
Gwamnan jihar Ebonyi Nweze Umahi, cikin gwamnoni 3 da suka jhalarc taron ta yanar gizo ya bayyana cewa ana bukatar goyon bayan kungiyoyin ci gaba domin inganta ayyukan.
Hukumar cigaba na DAI ita ta kaddamar da aikin tare da sauran kungiyoyin Najeriya don tattara bayanai da ayyuka gna tabbatar da cewa abokn huldarta sun samu bayanai da ungiyoyi.
