Shugaban Kasar Najeriya Yayi Buda Baki Da Sugabannin Jihar Zamfara A Makka

Shugaban kasar Najeriya Muhammadu Buhari yayi buda baki da gwamnan jihar Zamfara Abdulaziz Yari da sarkin Maradun, Garba Tambari ranar lahadi a kasar makka.

Mataimakin shugaban kasar na musamman ta fannin yada labarai da hulda da jama’a Garba Shehu ne ya bayyana hakan a Abuja ranar Lahadi.

Yayin shan ruwa shugaban ya bayyana rashin dadin dadin yadda ake rasa rayuka da dukiyoyi a jihar Zamfara sakamakon hare-haren da suke fama dasu na yan bindiga.

Sarkin Maradun ya jagoranci addu’ar da akayi yiwa wadanda harin ya ritsa dasu a jihar Zamfara da kasar najeriya gaba daya.

Shehu ya kara da cewa shugaban ya samu rakiyar shugaban ofishin jakadancin Najeriya a kasar Saudiya Justice Isa Dodo da kuma ma’aikatansa.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *