Dandal Kura Radio International Kanuri: Kowu’o Fal Kanuri Milion Mew’wu Kla
Kanuri Miliyan Goma, Murya Daya
Dandal Radio 98.9FM Voice for Peace
Dandal Kura FM 98.9 Kowo’u nabtu N3l3fay3
Dandal Kura FM 98.9 Muryan Zaman Lafiya

--:--
--:--
  • FM Stream
  • Shortwave

Shugaban Kasar Najeriya Yayi Buda Baki Da Sugabannin Jihar Zamfara A Makka

buhari-talkingsmall
Share on facebook
Share on google
Share on twitter
Share on linkedin

Shugaban kasar Najeriya Muhammadu Buhari yayi buda baki da gwamnan jihar Zamfara Abdulaziz Yari da sarkin Maradun, Garba Tambari ranar lahadi a kasar makka.

Mataimakin shugaban kasar na musamman ta fannin yada labarai da hulda da jama’a Garba Shehu ne ya bayyana hakan a Abuja ranar Lahadi.

Yayin shan ruwa shugaban ya bayyana rashin dadin dadin yadda ake rasa rayuka da dukiyoyi a jihar Zamfara sakamakon hare-haren da suke fama dasu na yan bindiga.

Sarkin Maradun ya jagoranci addu’ar da akayi yiwa wadanda harin ya ritsa dasu a jihar Zamfara da kasar najeriya gaba daya.

Shehu ya kara da cewa shugaban ya samu rakiyar shugaban ofishin jakadancin Najeriya a kasar Saudiya Justice Isa Dodo da kuma ma’aikatansa.

Related stories

Leave a Reply