Dandal Kura Radio International Kanuri: Kowu’o Fal Kanuri Milion Mew’wu Kla
Kanuri Miliyan Goma, Murya Daya
Dandal Radio 98.9FM Voice for Peace
Dandal Kura FM 98.9 Kowo’u nabtu N3l3fay3
Dandal Kura FM 98.9 Muryan Zaman Lafiya

--:--
--:--
  • FM Stream
  • Shortwave

Najeriya: Masu Ruwa Da Tsaki Na Yankin Arewa Maso Gabas Sun Bukaci Da A Karawa Jami’an Tsaro albashi

Summit
Share on facebook
Share on google
Share on twitter
Share on linkedin

Masu ruwa da tsaki a yankin Arewa maso Gabas a yayin taro game da matsalolin tsaro sun bukaci gwamnatin tarayya  da ta ‘kara kudaden da dakarun soji, jami’an ‘yan sanda da ma sauran jami’an tsaro suke samu domin yaki da ta’addanci da kuma sauran nau’ikan ta’addanci a yankin Arewa maso Gabas.

Daga ‘karshe yayin taron kwana da aka gudanar a dakin taron na Multipurpose dake gidan gwamnati anan birnin Maiduguri an cimma matsaya game da wasu batutuwa sha hudu.

Da yake jawabi gwamnan jiha Farfesa Babagana Umara Zulum ya bukaci dakarun soji, jami’in ‘yan sanda da ma sauran jami’an tsaro da su bada hadin kai domin a cigaba da ya‘kar ta’addanci.

Mahalarta taron sun bayyana cewa akwai bukatar hukumar raya yankin Arewa maso Gabas ta tallafawa gwamnonin Arewa maso Gabas, da kuma samarda kayayyan aiki ga jami’an ‘yan sanda da kuma sauran jami’an tsaro.

Taron ya kuma ‘karawa mahukunta a matakai daban-daban ‘kwarin gwiwa da zauna teburin sulhu da ‘yan ta’adda saboda hakan zai kasance mafi a’ala ga sauran wadanda suke da niyyar mika wuya.

Related stories

Leave a Reply