Kamaru: Kwamitin Taron Yan A Ware Ya Kara Wa’adin Taron Zuwa Nuwamba

Kwamitin da ya shirya taron gama gari na yan a ware ya dage taron zuwa 19 ga watan Nuwamba ba tare da bayyana dalilin hakan ba.

Kwamitin yace yana ta jiran a bashi damar gudanar taron bayan ya mika takardar neman izini, sunce suna kiran kasashen duniya dasu ci gaba da basu hadin kai da taimako.

Za dai a iya tunawa masu shirya taron wanda Emeritus Archbishop yake jagoranta har sun isa Bua a hutun mako don jiran a basu damar wanda har yanzu shiru.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *