Mazauna Garin Maiduguri Sunyi Kira Ga Gwamnatin Jihar Borno Da A Bude Hanyar Maiduguri Zuwa Damboa

Maiduguri-City-Gate-Nigeria_0 (1)
Share on facebook
Share on google
Share on twitter
Share on linkedin

Mazauna garin Maiduguri sunyi kira ga gwamnatin jihar Borno domin ske bude hanyar Maiduguri zuwa Damboa domin samun damar kai kayaki zuwa kasuwanni a kudancin jihar Borno.

Hajiya Fati Abubakar ita tayi kira a cikin shirin gidan radio Dandal Kura na koken masu sauraro inda tace yan kasuwa suna wahala wajen kai kayaki daga Maiduguri zuwa sauran wurare a kudancin jihar Borno.

Tace kasuwanci ta hanyar Maiduguri zuwa Damboa yafi sauki, amma a yanzu rufe hanyar da akayi yana sanya yin kwanaki a hanya kafin a isa inda ake so.

Ta kara dacewa suna asarar kayakin su kafin su isa inda suke a bukata, dan haka tayi kira ga gwamnatin jihar Borno da ta bude hanyar domin inganta kasuwancin su.

Download Our App from the Google Play Store

--:--
--:--
  • FM Stream
  • Shortwave

--:--
--:--
  • FM Stream
  • Shortwave

Latest news

Leave a Reply