Hafsan Sojojin Najeriya Sun Dukufar Wajen Kawo Karshen Ta’addanci

Hafsan sojin kasa na Najeriya Attahiru Ibrahim ya sake jaddada irin goyon bayan shuagba Buhari da kuma na rundunar sojan Najeriya wajen kawo karshe ta’addancin BokoHaram a Najeriya.

Ya bayyana hakan ne yayin tattaunawa da yan jaridu bayan ya kammala taro da manya-manyan ma’aikatan rundunar OLD a barikin Maimalari na Maiduguri.

Yace yana yawaita ziyara hedikwatan rundunar old ne domin basu kaimi da kuma nuna irin bada hankalin da hafsan yayi ga rundunar a yakar ta’addanci da sukeyi inda ya kuma albishirin cewa, shugaba Buhari zai bada duk wani abu na bukata a yakar ta’addancin.

A game da hare-haren kwanan nan day an kungiyar Boko Haram suka kai kan wasu runduna a yankin rewa maso gabaas, yace a okuta da dama rundunar tana samun nasara akan ayyukan yan ta’adda kuma yace hakika Najeriya zata shafe yan ta’adda a Najeriya.