Dandal Kura Radio International Kanuri: Kowu’o Fal Kanuri Milion Mew’wu Kla
Kanuri Miliyan Goma, Murya Daya
Dandal Radio 98.9FM Voice for Peace
Dandal Kura FM 98.9 Kowo’u nabtu N3l3fay3
Dandal Kura FM 98.9 Muryan Zaman Lafiya

--:--
--:--
  • FM Stream
  • Shortwave

Ebola ta Kashe Fiye Da Mutane 1,000 A Kasar Congo

ebola virus
Share on facebook
Share on google
Share on twitter
Share on linkedin

Fiye da mutane 1,000 suka rasu daga barkewar cutar Ebola a kasar Congo wanda wannan shine karo na biyu da yake da muni a tarihi.

Ministan lafiya Oly Ilunga yace cutar ta lashe rayuka wanda ya fara tun watan Augusta. Cutar ta fara ne tun shekarar 2014 zuwa 2016 a yammacin Afrika a Guinea, Sierra Leone and Liberia wadda ta kashe fiye da mutane 11,000 inda ta yadu har zuwa iyakar Uganda da Rwanda inda a watan Afrilu kungiyar lafiya ta duniya tace kar a sata acikin ciwon gaggawa a duniya.

An sha kai hare hare a guraren da ake bada maganin Ebola inda kungiyoyi masu zaman kansu suka kwashe ma’aikatan suinda suka bar ma’aikatan gwamnati kawai.

An kai kimanin hare-hare 119 tun watan junairu inda 42 kan kayan aikin lafiya, 85 kuma kan ma’aikatan lafiay. Inda aka kashe wasu, wasu kuma suka samu raunuka.

Related stories

Leave a Reply